Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya yi maraba da dokar hana duk bukukuwan Sallah a jihar yayin gudanar da bukukuwan Sallah da rundunar ‘yan sandan jihar ta sanar.
A ranar Talata ne rundunar ‘yan sandan Kano ta sanar da dakatar da bukukuwan saboda dalilai na tsaro, kwanaki kadan bayan Sarkin Kano na 16, Malam Muhammadu Sanusi II, ya fitar da takardar gayyato hakimai da mahayan dawakai domin halartar bukukuwan Sallah da ake gudanarwa duk shekara.