DCL Hausa Radio
Kaitsaye

PDP ta roki Shugaba Tinubu da ya sake bita kan farashin litar fetur da na lantarki a Nijeriya

-

Jam’iyyar PDP a Nijeriya ta yi kira ga Shugaba Tinubu da ya sake duba dukkanin tsare-tsaren da suka zama alakakai ga jama’ar kasar.

Sakataren Yada Labarai na jam’iyyar PDP, Mr Debo Ologunagba ne ya gabatar da wannan kokon barar a cikin sakon barka da sallah da ya aike wa ‘ya’yan jam’iyyar.

Google search engine

Jam’iyyar ta roki gwamnati da ta rage farashin man fetur, kudin wutar lantarki da wasu kudaden da ake cajin mutane.

Haka kuma sanarwar ta kara jan hankalin Shugaba Tinubu da ya yi amfani da shekaru 2 da suka rage masa wajen inganta rayuwar ‘yan Nijeriya.

Jam’iyyar ta kuma yi kira ga ‘yan Nijeriya da su kasance ‘yan kasa na gari da kuma dagewa da addu’a da kuma yin tawakkali duk da matsin tattalin arzikin da ake fama da shi da kuma matsalolin tsaro da ya addabi kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

George Akume Har Yanzu Shi Ne Sakataren Gwamnatin Tarayya – Fadar Shugaban Kasa

Fadar Shugaban Nijeriya ta musanta jita-jitar da ke yawo cewa an sauke Sanata George Akume daga matsayin Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF). A wata sanarwa da mai...

Yawaita buga sabbin takardun kudi da da aka rika yi a gwamnatin Buhari ne ya gurgunta darajar Naira – Oshiomhole

Sanata Adams Oshiomhole, ya zargi tsohuwar gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari da taka raws wajen gurgunta tattalin arziki Nijeriya Ya bayyana hakan a wani taro...

Mafi Shahara