Jam’iyyar PDP a Nijeriya ta yi kira ga Shugaba Tinubu da ya sake duba dukkanin tsare-tsaren da suka zama alakakai ga jama’ar kasar.
Sakataren Yada Labarai na jam’iyyar PDP, Mr Debo Ologunagba ne ya gabatar da wannan kokon barar a cikin sakon barka da sallah da ya aike wa ‘ya’yan jam’iyyar.
Jam’iyyar ta roki gwamnati da ta rage farashin man fetur, kudin wutar lantarki da wasu kudaden da ake cajin mutane.
Haka kuma sanarwar ta kara jan hankalin Shugaba Tinubu da ya yi amfani da shekaru 2 da suka rage masa wajen inganta rayuwar ‘yan Nijeriya.
Jam’iyyar ta kuma yi kira ga ‘yan Nijeriya da su kasance ‘yan kasa na gari da kuma dagewa da addu’a da kuma yin tawakkali duk da matsin tattalin arzikin da ake fama da shi da kuma matsalolin tsaro da ya addabi kasar.