DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar wakilan Nijeriya ta wanke kasar Togo daga zargin badakalar digirin bogi

-

Majalisar wakilan Nijeriya ta wanke jamhuriyar Togo daga zargin bada shedar digirin bogi, biyo bayan cece-kuce da ya mamaye fannin ilimin kasar a kwanakin da suka gabata.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da kwamitin majalisar da ke kula da koke-koken jama’a ya mayar da hankalin kan binciken jamhuriyar Benin, inda ake zargin ana bayar da jabun satifiket na digiri kamar ruwa.

Google search engine

Shugaban kwamitin, Bitrus Laori ne ya bayyana hakan yayin wani zaman da ya gudana a Abuja ranar Juma’a, biyo bayan korafin da wata kungiya ‘Sovereign Legal Practitioners’ suka shigar a madadin masu ruwa da tsaki a harkar ilimi.

Takardar koken ta nemi yin bincike kan sanarwar da ma’aikatar ilimi ta Nijeriya ta fitar a shekarar da ta gabata, inda take zargin kasashen Togo da Jamhuriyar Benin da bayar da digirin bogi.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu is a highly skilled and experienced broadcast journalist and fact-checker. Ukashatu has over five years of experience in writing, editing, and presenting news and program content for radio and television. As a dedicated and hardworking professional, He is committed to upholding the values of accuracy, fairness, balance, independence, and accountability in her reporting and programs.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kiran kungiyar NNPYA na neman Tinubu ya zabe ni a takarar mataimaki a 2027 bai dace ba yanzu – Sanata Barau Jibrin

Sanata Barau I. Jibrin, Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, ya ce kiraye-kirayen da kungiyar matasan jam’iyyar APC na Arewa (NNPYA) ke yi na a zabe shi...

Yawancin ma su rawar kafar kawar da Tinubu ba domin jin ƙan jama’a suke ba – Shehu Sani

Tsohon Sanata mai wakiltar Kaduna ta tsakiya kuma mai rajin kare hakkin dan Adam, Shehu Sani, ya ce yawancin ma su sukar takun gwamnatin Tinubu...

Mafi Shahara