Ministan Sufurin Jiragen Sama da Ci gaban Sararin Samaniya, Festus Keyamo, ya bayyana cewa sabuwar jam’iyyar siyasa ta ADA ba zata iya zama barazana ga jam’iyya mai mulki, APC, ba.
Keyamo ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X, inda ya ce kafa jam’iyyar ADA ba ta yi kama da irin haɗin gwiwar da aka yi wajen gina APC a shekarar 2013 ba.
Jam’iyyar ADA na samun goyon bayan wasu fitattun ‘yan siyasa, ciki har da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, da tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai.
Jaridar Dailytrust ta ruwaito cewa tuni aka mika takardar neman rajistar jam’iyyar ga Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) a ranar 19 ga Yuni, 2025.