Kungiyar magoya bayan shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ta Disciples of Jagaban ta ce ba a makance ta ke nuna goyon baya ga shugaban ba, domin kuwa ta na da hujjoji.
Cikin wata sanarwa da da shugaban kungiyar na kasa Abdulhakeem Adwgoke Alawuje ya fitar, kungiyar ta bayyana cewa ta fara goyon bayan Bola Tinubu ne tun zamanin baya, a lokacin da yake rainon kudirinsa na zama shugaban Nijeriya.
Kungiyar ta DOJ, ta kafa hujjoji da cewa tana nuna goyon baya ne bisa tsare tsaren Tinubu kan tattalin arziki, musamman cire tallafin man fetur mai cike da zargin damfara.
Ta kuma bukaci yan Nijeriya su yi watsi da duk wani shiri da yan adawa ke yi da sunan hadakar jam’iyyu, domin a cewar ta yunkuri ne kawai na lalata kyakkyawan shirin da Tinubu ya yi wa Nijeriya da al’ummarta.