DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Muna da hujja ba a makance muke goyon Tinubu ba – Kungiyar Disciples of Jagaban

-

Kungiyar magoya bayan shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ta Disciples of Jagaban ta ce ba a makance ta ke nuna goyon baya ga shugaban ba, domin kuwa ta na da hujjoji.

Cikin wata sanarwa da da shugaban kungiyar na kasa Abdulhakeem Adwgoke Alawuje ya fitar, kungiyar ta bayyana cewa ta fara goyon bayan Bola Tinubu ne tun zamanin baya, a lokacin da yake rainon kudirinsa na zama shugaban Nijeriya.

Google search engine

Kungiyar ta DOJ, ta kafa hujjoji da cewa tana nuna goyon baya ne bisa tsare tsaren Tinubu kan tattalin arziki, musamman cire tallafin man fetur mai cike da zargin damfara.

Ta kuma bukaci yan Nijeriya su yi watsi da duk wani shiri da yan adawa ke yi da sunan hadakar jam’iyyu, domin a cewar ta yunkuri ne kawai na lalata kyakkyawan shirin da Tinubu ya yi wa Nijeriya da al’ummarta.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu is a highly skilled and experienced broadcast journalist and fact-checker. Ukashatu has over five years of experience in writing, editing, and presenting news and program content for radio and television. As a dedicated and hardworking professional, He is committed to upholding the values of accuracy, fairness, balance, independence, and accountability in her reporting and programs.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Rundunar sojin Nijeriya ta sulhunta kabilun da ke rikici a Taraba

By Salisu Ado Sulaiman Rundunar sojin kasan Nijeriya ta jagoranci zaman sulhu tsakanin kabilun da ke rikici a jihar Taraba. Kwamandan rundunar Operation Whirl Punch Brigadier Janar...

Shugaban kasar Uganda mai shekaru 80, zai sake tsayawa takara bayan shafe shekara 39 kan mulki

Jam'iyyar NRM mai mulki a kasar Uganda ta ce shugaban kasar Yoweri Museveni zai sake neman tsayawa takara a zaben da za a gudanar a...

Mafi Shahara