Tsohon gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa jiga-jigan ‘yan adawa na son fitowa da sabuwar jam’iyyar ne gabanin zaben 2027, saboda kutsen da ‘yan koren gwamnatin APC suka yi a cikin jam’iyyun da ake da su a yanzu.
Ya ba da misali da rikicin cikin gida dake faruwa a jam’iyyun PDP da LP da kuma NNPP.
A wata hira da gidan talabijin na Arise TV, El-Rufai ya ce bukatar yin rajistar jam’iyyar ADA da suka mika ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC wata dabara ce ta tsaftace hadakar daga duk wani kutse don kalubalantar shugaba Bola Tinubu a zaben dake tafe.
Sai dai El-Rufai ya zargi gwamnatin APC wajen kawo cikas ga yunkurin yin rijistar jam’iyyar ‘yan adawa.