DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Za mu yi sabuwar jam’iyya ne saboda gwamnatin APC ta gurbata jam’iyyun adawa – Nasir El-Rufa’i

-

Tsohon gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa jiga-jigan ‘yan adawa na son fitowa da sabuwar jam’iyyar ne gabanin zaben 2027, saboda kutsen da ‘yan koren gwamnatin APC suka yi a cikin jam’iyyun da ake da su a yanzu.

Ya ba da misali da rikicin cikin gida dake faruwa a jam’iyyun PDP da LP da kuma NNPP.

Google search engine

A wata hira da gidan talabijin na Arise TV, El-Rufai ya ce bukatar yin rajistar jam’iyyar ADA da suka mika ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC wata dabara ce ta tsaftace hadakar daga duk wani kutse don kalubalantar shugaba Bola Tinubu a zaben dake tafe.

Sai dai El-Rufai ya zargi gwamnatin APC wajen kawo cikas ga yunkurin yin rijistar jam’iyyar ‘yan adawa.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu is a highly skilled and experienced broadcast journalist and fact-checker. Ukashatu has over five years of experience in writing, editing, and presenting news and program content for radio and television. As a dedicated and hardworking professional, He is committed to upholding the values of accuracy, fairness, balance, independence, and accountability in her reporting and programs.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Muna da hujja ba a makance muke goyon Tinubu ba – Kungiyar Disciples of Jagaban

Kungiyar magoya bayan shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ta Disciples of Jagaban ta ce ba a makance ta ke nuna goyon baya ga shugaban ba,...

Rundunar sojin Nijeriya ta sulhunta kabilun da ke rikici a Taraba

By Salisu Ado Sulaiman Rundunar sojin kasan Nijeriya ta jagoranci zaman sulhu tsakanin kabilun da ke rikici a jihar Taraba. Kwamandan rundunar Operation Whirl Punch Brigadier Janar...

Mafi Shahara