DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ba mu tsawaita wa’adin hidimta wa kasar matashiyar da ta caccaki Shugaba Tinubu ba – NYSC

-

Hukumar NYSC ta karyata zargin tsawaita wa wata ‘yar bautar ƙasa daga Legas, Rita Uguamaye (Raye), aikin watanni biyu saboda sukar gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.

Raye ta shahara a kafafen sada zumunta bayan ta wallafa bidiyo a TikTok tana koka da tsadar rayuwa da hauhawar farashi, tare da sukar Tinubu da kiran sa “shugaba mara tausayi.”

Google search engine

Daga baya, Raye ta ce ana yi mata barazana daga jami’an NYSC saboda bidiyon, inda ta ƙi goge shi tana mai cewa ta faɗi gaskiya ne.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa biyo bayan zargin da Raye ta yi, mutane da dama ciki har da tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar da ɗan gwagwarmayar kare haƙƙin ɗan adam, Omoyele Sowore, sun yi Allah-wadai da barazanar da aka ce ana yi mata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara