DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ba mu tsawaita wa’adin hidimta wa kasar matashiyar da ta caccaki Shugaba Tinubu ba – NYSC

-

Hukumar NYSC ta karyata zargin tsawaita wa wata ‘yar bautar ƙasa daga Legas, Rita Uguamaye (Raye), aikin watanni biyu saboda sukar gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.

Raye ta shahara a kafafen sada zumunta bayan ta wallafa bidiyo a TikTok tana koka da tsadar rayuwa da hauhawar farashi, tare da sukar Tinubu da kiran sa “shugaba mara tausayi.”

Google search engine

Daga baya, Raye ta ce ana yi mata barazana daga jami’an NYSC saboda bidiyon, inda ta ƙi goge shi tana mai cewa ta faɗi gaskiya ne.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa biyo bayan zargin da Raye ta yi, mutane da dama ciki har da tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar da ɗan gwagwarmayar kare haƙƙin ɗan adam, Omoyele Sowore, sun yi Allah-wadai da barazanar da aka ce ana yi mata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon Gwamnan jihar Kwara Cornelius Adebayo ya rasu

Tsohon Gwamnan jihar Kwara kuma Ministan Sadarwa na baya, Cornelius Adebayo, ya rasu yana da shekara 84 a Abuja da safiyar Laraba nan. Babban dansa Oluwasegun,...

An karrama ma’aikacin gwamnatin Jigawa a Saudiyya bisa dawo da kuɗin da ya tsinta

Wani ma’aikacin gudanarwa a Saudiyya, Muhammed Salalah, ya mika kwafin Alkur’ani Mai Tsarki ga Daraktan Rediyon Jigawa, Malam Isma’il Babura, a matsayin kyauta mai daraja...

Mafi Shahara