DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kiran kungiyar NNPYA na neman Tinubu ya zabe ni a takarar mataimaki a 2027 bai dace ba yanzu – Sanata Barau Jibrin

-

Sanata Barau I. Jibrin, Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, ya ce kiraye-kirayen da kungiyar matasan jam’iyyar APC na Arewa (NNPYA) ke yi na a zabe shi a matsayin mataimakin Tinubu a 2027 ba su dace da lokaci ba.

A wata sanarwa da mai ba shi shawara na musamman kan yada labarai, Ismail Mudashir, ya fitar, Barau ya bukaci matasan su daina kamfen din su maida hankali kan tallafa manufar Shugaba Tinubu ta Renewed Hope Agenda ga Jama’ar kasa.

Google search engine

Jaridar Daily Trust ta ruwaito, mataimakin shugaban majalisar ECOWAS din ya ce, “Idan har kuna goyon bayana da gaske, ku daina wannan kiraye-kirayen da ba su dace ba, ku mara wa Shugaba Tinubu baya don dawo da martabar ƙasar nan.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

INEC na duba buƙatun kungiyoyi 110 da ke neman rigista a matsayin jam’iyyun siyasa a Najeriya

Hukumar zabe ta kasa INEC ta bayyana cewa ta karɓi wasikun buƙatun rajistar sabbin jam’iyyu 110 daga kungiyoyi daban-daban har zuwa Litinin, 23 ga watan...

PDP ta maido wa Samuel Anyanwu mukaminsa na sakataren jam’iyyar na kasa

PDP ta maido wa Samuel Anyanwu mukaminsa na sakataren jam'iyyar na kasa Jam’iyyar PDP ta dawo da Samuel Anyanwu a matsayin sakataren jam’iyya na kasa bayan...

Mafi Shahara