DCL Hausa Radio
Kaitsaye

PDP ta maido wa Samuel Anyanwu mukaminsa na sakataren jam’iyyar na kasa

-

PDP ta maido wa Samuel Anyanwu mukaminsa na sakataren jam’iyyar na kasa

Jam’iyyar PDP ta dawo da Samuel Anyanwu a matsayin sakataren jam’iyya na kasa bayan ganawarta da hukumar INEC a ranar Talata.

Google search engine

Shugaban rikon kwarya na PDP, Umar Damagum, ya bayyana hakan a taron manema labarai a Abuja, inda ya ce Anyanwu zai ci gaba da aiki a matsayin sakataren kamar yadda gidan Talabijin na Channels ya tabbatar.

Jam’iyyar ta kuma soke taron NEC da aka shirya gudanarwa a ranar 30 ga Yuni, inda ta maye gurbinsa da taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar.

A baya hukumar zaben Nijeriya INEC ta ce ba za ta halarci taron NEC na PDP ba saboda rikicin shugabancin sakataren jam’iyyar da kuma sabanin da ke cikin sa hannun takardun da aka aikewa hukumar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

INEC na duba buƙatun kungiyoyi 110 da ke neman rigista a matsayin jam’iyyun siyasa a Najeriya

Hukumar zabe ta kasa INEC ta bayyana cewa ta karɓi wasikun buƙatun rajistar sabbin jam’iyyu 110 daga kungiyoyi daban-daban har zuwa Litinin, 23 ga watan...

Tsohon Gwamnan jihar Kwara Cornelius Adebayo ya rasu

Tsohon Gwamnan jihar Kwara kuma Ministan Sadarwa na baya, Cornelius Adebayo, ya rasu yana da shekara 84 a Abuja da safiyar Laraba nan. Babban dansa Oluwasegun,...

Mafi Shahara