DCL Hausa Radio
Kaitsaye

PDP ta maido wa Samuel Anyanwu mukaminsa na sakataren jam’iyyar na kasa

-

PDP ta maido wa Samuel Anyanwu mukaminsa na sakataren jam’iyyar na kasa

Jam’iyyar PDP ta dawo da Samuel Anyanwu a matsayin sakataren jam’iyya na kasa bayan ganawarta da hukumar INEC a ranar Talata.

Google search engine

Shugaban rikon kwarya na PDP, Umar Damagum, ya bayyana hakan a taron manema labarai a Abuja, inda ya ce Anyanwu zai ci gaba da aiki a matsayin sakataren kamar yadda gidan Talabijin na Channels ya tabbatar.

Jam’iyyar ta kuma soke taron NEC da aka shirya gudanarwa a ranar 30 ga Yuni, inda ta maye gurbinsa da taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar.

A baya hukumar zaben Nijeriya INEC ta ce ba za ta halarci taron NEC na PDP ba saboda rikicin shugabancin sakataren jam’iyyar da kuma sabanin da ke cikin sa hannun takardun da aka aikewa hukumar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara