DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Yawancin ma su rawar kafar kawar da Tinubu ba domin jin ƙan jama’a suke ba – Shehu Sani

-

Tsohon Sanata mai wakiltar Kaduna ta tsakiya kuma mai rajin kare hakkin dan Adam, Shehu Sani, ya ce yawancin ma su sukar takun gwamnatin Tinubu ba domin jin ƙan jama’a suke ba, sai don fushin an hana su mukami da gaza cimma muradun siyasa.

A wata hira da ya yi da gidan Talabijin na Channels, ya ce yawancin ’yan adawan suna daga cikin tsaffin masu mulki ne tun 1999 da suka rasa matsayi yanzu.

Google search engine

Ya ƙara da cewa babu bambanci a tsakanin su da masu mulki, dukkansu daga ƙungiyar ’yan siyasar elite su ka fito.

Shehu Sani ya kuma ce bai dace a dora wa Tinubu laifin rikicin da ke cikin jam’iyyun adawa ba, inda ya soki yunƙurin kafa kawance na siyasa da Atiku da sauran manyan ’yan siyasa ke yi don 2027.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

INEC na duba buƙatun kungiyoyi 110 da ke neman rigista a matsayin jam’iyyun siyasa a Najeriya

Hukumar zabe ta kasa INEC ta bayyana cewa ta karɓi wasikun buƙatun rajistar sabbin jam’iyyu 110 daga kungiyoyi daban-daban har zuwa Litinin, 23 ga watan...

PDP ta maido wa Samuel Anyanwu mukaminsa na sakataren jam’iyyar na kasa

PDP ta maido wa Samuel Anyanwu mukaminsa na sakataren jam'iyyar na kasa Jam’iyyar PDP ta dawo da Samuel Anyanwu a matsayin sakataren jam’iyya na kasa bayan...

Mafi Shahara