DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Yawancin ma su rawar kafar kawar da Tinubu ba domin jin ƙan jama’a suke ba – Shehu Sani

-

Tsohon Sanata mai wakiltar Kaduna ta tsakiya kuma mai rajin kare hakkin dan Adam, Shehu Sani, ya ce yawancin ma su sukar takun gwamnatin Tinubu ba domin jin ƙan jama’a suke ba, sai don fushin an hana su mukami da gaza cimma muradun siyasa.

A wata hira da ya yi da gidan Talabijin na Channels, ya ce yawancin ’yan adawan suna daga cikin tsaffin masu mulki ne tun 1999 da suka rasa matsayi yanzu.

Google search engine

Ya ƙara da cewa babu bambanci a tsakanin su da masu mulki, dukkansu daga ƙungiyar ’yan siyasar elite su ka fito.

Shehu Sani ya kuma ce bai dace a dora wa Tinubu laifin rikicin da ke cikin jam’iyyun adawa ba, inda ya soki yunƙurin kafa kawance na siyasa da Atiku da sauran manyan ’yan siyasa ke yi don 2027.

4 COMMENTS

  1. To, na yarda da maganar comrade. Amma ina so in tambaye shi, shi yana ganin cewa, Tinubu ya cancanta ya cigaba da mulki bisa tamarin tsarin salon mulkin sa? Kuma shi mulkin na shugaba Tinubu a hangen comrade Sani, yana tausaya wa jama’a, musamman talaKawa?

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara