DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Bayan shafe watanni 23, Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC

-

Ta dai tabbata, Abdullahi Umar Ganduje ya yi murabus daga shugabancin jam’iyyar APC ta kasa.

Tsohon Gwamnan jihar Kanon ya ajiye mukamin nasa da yammacin Juma’ar nan, kamar yadda gidan talabijin na TVC ya rawaito. Hakan na zuwa ne ‘yan kwanakin bayan takaddamar da ta biyo bayan babban taron jam’iyyar na shiyyar arewa maso Gabas a Gombe, inda nuna goyon bayan takarar shugaba Tinubu a jam’iyyar a azben 2027 ba tare da ayyana Kashim Shettima a matsayin mataimakinsa ba da gandujen ya yi, ya janyo cece-kuce.

Google search engine

Rahotanni sun ce Dr. Ganduje ya gabatar da uzurin rashin lafiya a matsayin dalilin saukarsa daga kujerar. To amma jaridar Daily Nigerian ta ruwaito cewa jam’iyyar APC ta lallashi Dr. Abdullahi Umar Ganduje da ya ajiye mukamin nasa domin bai wa jam’iyyar damar tsara dabarun tunkarar zaben 2027.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara