DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Bayan shafe watanni 23, Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC

-

Ta dai tabbata, Abdullahi Umar Ganduje ya yi murabus daga shugabancin jam’iyyar APC ta kasa.

Tsohon Gwamnan jihar Kanon ya ajiye mukamin nasa da yammacin Juma’ar nan, kamar yadda gidan talabijin na TVC ya rawaito. Hakan na zuwa ne ‘yan kwanakin bayan takaddamar da ta biyo bayan babban taron jam’iyyar na shiyyar arewa maso Gabas a Gombe, inda nuna goyon bayan takarar shugaba Tinubu a jam’iyyar a azben 2027 ba tare da ayyana Kashim Shettima a matsayin mataimakinsa ba da gandujen ya yi, ya janyo cece-kuce.

Google search engine

Rahotanni sun ce Dr. Ganduje ya gabatar da uzurin rashin lafiya a matsayin dalilin saukarsa daga kujerar. To amma jaridar Daily Nigerian ta ruwaito cewa jam’iyyar APC ta lallashi Dr. Abdullahi Umar Ganduje da ya ajiye mukamin nasa domin bai wa jam’iyyar damar tsara dabarun tunkarar zaben 2027.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tarihin marigayi Aminu Dantata

Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un. Najeriya ta yi babban rashi – na dattijo, attajiri, mai hangen nesa da zuciya mai tausayi: Alhaji Aminu Alhassan...

Indomie ta kaddamar da gangami don tallafa wa nasarar iyaye da ‘ya’Ć´ansu

Indomie, shahararren kamfanin taliyar Indomie a Najeriya, ya ƙaddamar da sabon gangami mai taken “Ingantaccen Abinci Domin Nasara”. Wannan gangami yana jaddada muhimmancin abinci mai...

Mafi Shahara