DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Mun magance sabaninmu, yanzu a shirye nake nayi aiki da Fubara – Nyesome Wike

-

Ministan birnin tarayya Abuja Nyesom Wike, ya bayyana cewa rikicin siyasa tsakaninsa da tsohon yaronsa ya kawo karshe kuma zaman lafiya ya dawo a jihar Rivers.

Wike ya ce shi da dakataccen gwamnan jihar, Siminalayi Fubara, da ‘yan majalisar dokokin jihar sun sasanta rashin jituwar da ke tsakaninsu.

Google search engine

Ya bayyana hakan ne biyo bayan wata ganawa da shugaban kasa Bola Tinubu yayi da bangarorin a fadar shugaban kasa da ke Abuja a daren Alhamis.

Wike da Fubara dai sun dade suna takun saka a rikicin da ya barke a yankin Rivers, lamarin da ya taba majalisar dokokin jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tarihin marigayi Aminu Dantata

Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un. Najeriya ta yi babban rashi – na dattijo, attajiri, mai hangen nesa da zuciya mai tausayi: Alhaji Aminu Alhassan...

Bayan shafe watanni 23, Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC

Ta dai tabbata, Abdullahi Umar Ganduje ya yi murabus daga shugabancin jam'iyyar APC ta kasa. Tsohon Gwamnan jihar Kanon ya ajiye mukamin nasa da yammacin Juma'ar...

Mafi Shahara