DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Rundunar sojin saman Nijeriya sun yi ajalin ‘yan bindiga da dama a jihar Neja

-

Sojojin saman Nijeriya dake karkashin rundunar Operation Fansar yamma, sun yi luguden wuta ga ‘yan bindiga da suka kai hare-hare na baya-bayan nan a jihar Neja, tare da tallafi ta kasa daga sojojin kasar.

Harin wanda aka aiwatar tsakanin 24 zuwa 26 ga watan Yuni, 2025, an gudanar da su ne bisa ingantattun bayanan sirri, a cewar sanarwar da daraktan yada labarai na rundunar, Air Commodore Ehimen Ejodame, ya fitar ranar Juma’a a Abuja.

Google search engine

Ya ce rundunar, hadin gwiwa sauran hukumomin tsaro, sun gano ‘yan ta’adda masu kai hare-hare da satar shanu a yankunan Kakihun da Kumbashi.

Cikin hanzari rundunar ta tura da jirage domin kai hare-hare wanda aka yi nasara tare da lalata musu kayayyaki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tarihin marigayi Aminu Dantata

Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un. Najeriya ta yi babban rashi – na dattijo, attajiri, mai hangen nesa da zuciya mai tausayi: Alhaji Aminu Alhassan...

Bayan shafe watanni 23, Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC

Ta dai tabbata, Abdullahi Umar Ganduje ya yi murabus daga shugabancin jam'iyyar APC ta kasa. Tsohon Gwamnan jihar Kanon ya ajiye mukamin nasa da yammacin Juma'ar...

Mafi Shahara