Sojojin saman Nijeriya dake karkashin rundunar Operation Fansar yamma, sun yi luguden wuta ga ‘yan bindiga da suka kai hare-hare na baya-bayan nan a jihar Neja, tare da tallafi ta kasa daga sojojin kasar.
Harin wanda aka aiwatar tsakanin 24 zuwa 26 ga watan Yuni, 2025, an gudanar da su ne bisa ingantattun bayanan sirri, a cewar sanarwar da daraktan yada labarai na rundunar, Air Commodore Ehimen Ejodame, ya fitar ranar Juma’a a Abuja.
Ya ce rundunar, hadin gwiwa sauran hukumomin tsaro, sun gano ‘yan ta’adda masu kai hare-hare da satar shanu a yankunan Kakihun da Kumbashi.
Cikin hanzari rundunar ta tura da jirage domin kai hare-hare wanda aka yi nasara tare da lalata musu kayayyaki.