DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jaridar Punch ta gano hakikanin abin da ya sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC

-

Bayanai sun fara fita dalla-dalla kan dalilan da suka sa shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Ganduje, ya yi murabus daga mukaminsa a ranar Juma’a.

Rahoton da jaridar PUNCH ta samu daga majiya mai ƙarfi ya nuna cewa Ganduje ya ajiye mukaminsa ne saboda rahotannin cewa tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, na shirin shiga jam’iyyar APC.

Google search engine

Tun da misalin ƙarfe 3 na rana a ranar Juma’a, wasu da ke aiki a sakatariyar jam’iyyar ta ƙasa sun shaida wa jaridar cewa tsohon shugaban jam’iyyar ya fara barazanar yin murabus saboda yarjejeniyar da aka ce ta faru tsakanin Shugaba Bola Tinubu da Kwankwaso don shigar Kwankwaso jam’iyyar.

Wata majiya ta bayyana cewa duk manyan jami’an jam’iyyar, ciki ha da sakataren jam’iyya na ƙasa, Ajibola Basiru, sun yi ƙoƙarin hana Ganduje ajiye mukaminsa.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Manufofin Tinubu ne ke jan hankalin ‘yan siyasa zuwa APC – Gwamnan Nassarawa

Gwamnan jihar Nassarawa Abdullahi Sule ya ce guguwar sauyin sheka tsakanin 'yan siyasa da ake samu a baya bayan nan musamman ga masu shiga APC,...

Dan majalisar wakilan Nijeriya daga Benue ya fice daga PDP zuwa APC

Dan majalisar wakilan Nijeriya mai wakiltar Apa/Agatu da ke jihar Benue, Ojoma Ojotu ya fice daga jam’iyyar PDP tare da komawa APC. Bayanin sauya shekar dan...

Mafi Shahara