DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Murabus din Ganduje wata maƙarƙashiya ce aka shirya domin cire Shettima daga gwamnatin Tinubu – Zargin wasu mutanen Borno

-

Wasu daga cikin al’ummar jihar Borno sun zargi murabus din Ganduje a matsayin wata maƙarƙashiya da aka shirya domin a kawar da Kassim Shettima a gwamnatin Tinubu a zaben shekarar 2027, kamar yadda jaridar Premium Times ta rawaito.

A yammacin ranar Juma’a ne dai Ganduje ya yi murabus daga mukaminsa na shugabancin jam’iyyar APC, inda nan take aka rantsar da mataimakin shugaban jam’iyyar na kasa daga yankin (Arewa), Ali Dalori a matsayin shugaban riko.

Google search engine

Dalori dai ɗan asalin jihar Borno ne wadda ita ce jihar da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya fito.

Kodayake Ganduje ya ce ya yi murabus ne bisa dalilai na kula da lafiyarsa,

Sai dai jita-jita na nuna cewa ‘yan jam’iyyar ne suka tilasta masa yin murabus don ba da damar sake fasalin tsarin shugabancin jam’iyyar kafin babban zaben Nijeriya na shekarar 2027.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Yawaita buga sabbin takardun kudi da da aka rika yi a gwamnatin Buhari ne ya gurgunta darajar Naira – Oshiomhole

Sanata Adams Oshiomhole, ya zargi tsohuwar gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari da taka raws wajen gurgunta tattalin arziki Nijeriya Ya bayyana hakan a wani taro...

Jaridar Punch ta gano hakikanin abin da ya sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC

Bayanai sun fara fita dalla-dalla kan dalilan da suka sa shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Ganduje, ya yi murabus daga mukaminsa a ranar Juma’a. Rahoton...

Mafi Shahara