DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kai ya rabu kan taron NEC karo na 100 da jam’iyyar PDP za ta yi yau

-

Jam’iyyar PDP na shirin gudanar da babban taronta a yau Litinin 30 ga Yuni, 2025 a sakatariyar jam’iyyar ta kasa da ke Abuja, yayin da rikici ya kara ta’azzara tsakanin bangarori biyu na shugabancin jam’iyyar.

Rahoton Jaridar Daily Trust ya ambato bangaren shugaban riko na kasa, Umar Damagum, da Sanata Samuel Anyanwu sun bayyana taron a matsayin “Taron Caucus”, tare da gayyatar masu ruwa da tsaki.

Google search engine

Sai dai, mataimakin shugaban jam’iyyar na kudu, Amb. Taofeek Arapaja, tare da mambobi 11 na NWC, dake samun goyon bayan bangaren Gwamna Seyi Makinde na Oyo, wanda ya hada da gwamnonin Enugu, Bayelsa, Osun da Zamfara, da mambobin NWC 11 da wasu jiga-jigan jam’iyyar, sun dage cewa dole a gudanar da taron NEC kamar yadda aka tsara.

A daya bangaren kuma, tsohon Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike, wanda ke samun goyon bayan gwamnonin Plateau, Taraba, Adamawa, Bauchi da shugaban rikon kwarya Umar Damagum, na bukatar a dage taron kuma a maido da Anyanwu kan mukaminsa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Jam’iyyar ADC a Kaduna ta kori mataimakin shugabanta da wasu ‘ya’yanta 8

Jam'iyyar hadaka ta ADC mai hamayya a Nijeriya reshen Kaduna ta kori mataimakin shugabanta na jihar tare da wasu manyan jami'anta guda takwas, bayan samun...

Hukumar FRSC ta bayyana dalilan yawan afkuwar hadura a titunan Nijeriya

Hukumar kiyaye afkuwar hadura ta Nijeriya FRSC ta bayyana cewa a mafiya yawan lokuta rashin hakuri, gudun wuce sa'a tare da karya dokokin hanya ne...

Mafi Shahara