DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hukumar alhazan Nijeriya ta ce ta kammala jigilar dawo da alhazan bana

-

Hukumar kula da aikin hajji NAHCON ta ce ta kammala aikin dawo da alhazai gida daga kasar Saudiyya bayan kammala aikin Hajjin bana, 2025.

Jirgin karshen ya tashi daga birnin Jeddah da misalin karfe 10:30 na safiyar Talata, inda ya sauka a Kaduna dauke da mahajjata 87.

Google search engine

Aikin dawo da mahajjatan ya dauki kwanaki 17 tun bayan fara shi a ranar 13 ga watan Yuni, kuma ya gudana cikin nasara ba tare da wata matsala ba, kamar yadda wata sanarwa daga Fatima Sanda Usara jami’a a sashen yada labaran hukumar ta sanar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnan Bauchi ya sanya hannu kan dokar kirkirar sabbin masarautu 13 a fadin jihar

Gwamnan Bauchi Bala Muhammad ya sanya hannu kan dokar kirkirar sabbin masarautu 13 a fadin jihar. Daily Trust ta ruwaito cewa a lokacin da yake sanya...

Kenya da Senegal sun kulla yarjejeniyar shige da fice ba tare da biza ba

Gwamnatocin Kenya da Senegal sun bai wa juna damar shige da fice ga 'yan kasashensu ba tare da biza ba na tsawon kwanaki 90. DW Africa...

Mafi Shahara