Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya bayyana cewa duk wanda bai ganin nasarorin da shugaba Bola Tinubu ke samu ba, to lallai siyasar sa ta kai karshe.
Gidan talabijin na Channels ya ruwaito Wike na bayyana hakan a yayin kaddamar da ayyukan tituna daga Ushafa zuwa Bwari a Abuja, inda ya ce masu sukar tafiyar gwamnatin Tinubu suna kokarin raina ci gaban da ake samu.
Ya kara da cewa yawancin masu suka sun dade suna yawon jam’iyya tun daga 1999 ba tare da wani abin a zo a gani da suka samar ba, amma yanzu suna neman hana Tinubu damar yin aiki.
Ministan ya ce gwamnatin Tinubu tana aiwatar da ayyuka a sassa daban-daban na kasar, kuma duk wanda ya gaza gane hakan, ko dai makaho ne ko kuma son zuciya ne ya rufe masa ido.



