DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jam’iyyar Labour tsagin Julius Abure ta ba Peter Obi sa’o’i 48 ya fice daga jam’iyyar saboda shiga hadakar ADC

-

Jam’iyyar Labour karkashin jagorancin Julius Abure ta bai wa tsohon dan takarar shugaban kasa, Peter Obi, wa’adin sa’o’i 48 da ya fice daga jam’iyyar, bisa dalilin shiga hadakar jam’iyyun adawa da ke shirin kalubalantar APC a 2027.

A wata sanarwa da sakataren jam’iyyar na kasa, Obiora Ifoh, ya fitar a Abuja, ya ce ba su da hannu a cikin wannan hadaka, yana mai zargin cewa yawancin wadanda ke ciki suna fi ba da fifiko ga kare muradun kansu ba na jama’a ba.

Google search engine

Obiora ya ce jam’iyyar ba za ta lamunci kasancewa da ’yan siyasa masu fuska biyu ba, inda ya bukaci duk wani mamba da ya shiga hadakar jam’iyyun adawa da ya fice cikin sa’o’i 48 kamar yadda rahoton jaridar The Nation ya tabbatar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

’Yan majalisar wakilai bakwai daga Akwa Ibom sun sauya sheka zuwa APC

Ana cigaba da samun rahotannin sauyin sheka a majalisar wakilai, yayin da ’yan majalisa bakwai daga Jihar Akwa Ibom suka koma jam’iyyar APC. Wadanda suka...

Cibiyar taro ta Bola Tinubu ta samar da naira miliyan 650 cikin mako uku — Minista Wike

Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya bayyana cewa sabuwar Cibiyar taro ta Ƙasa da Ƙasa mai suna Bola Ahmed Tinubu da aka kaddamar kwanan...

Mafi Shahara