DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jam’iyyar Labour tsagin Julius Abure ta ba Peter Obi sa’o’i 48 ya fice daga jam’iyyar saboda shiga hadakar ADC

-

Jam’iyyar Labour karkashin jagorancin Julius Abure ta bai wa tsohon dan takarar shugaban kasa, Peter Obi, wa’adin sa’o’i 48 da ya fice daga jam’iyyar, bisa dalilin shiga hadakar jam’iyyun adawa da ke shirin kalubalantar APC a 2027.

A wata sanarwa da sakataren jam’iyyar na kasa, Obiora Ifoh, ya fitar a Abuja, ya ce ba su da hannu a cikin wannan hadaka, yana mai zargin cewa yawancin wadanda ke ciki suna fi ba da fifiko ga kare muradun kansu ba na jama’a ba.

Google search engine

Obiora ya ce jam’iyyar ba za ta lamunci kasancewa da ’yan siyasa masu fuska biyu ba, inda ya bukaci duk wani mamba da ya shiga hadakar jam’iyyun adawa da ya fice cikin sa’o’i 48 kamar yadda rahoton jaridar The Nation ya tabbatar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara