DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Buhari na murmurewa a jinyar da yake yi a London – Garba Shehu

-

Tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, mai shekara 82, na karɓar magani a birnin Landan tun daga watan Afrilu.

Buhari, wanda ya sauka daga mulki a 2023 bayan kammala wa’adin mulki na biyu, ya fara tafiya ne don duba lafiyarsa, amma daga bisani ya kamu da rashin lafiya tare da shafe kwanaki a dakin kulawa ta musamman (ICU).

Google search engine

DW Africa ta ruwaito mai magana da yawunsa, Garba Shehu, ya tabbatar da cewa Buhari na fama da rashin lafiya kuma yana jinya a Landan, amma bai bayyana asalin cutar ko asibitin da yake kwance ba.

Ana sa ran zai dawo gida Najeriya da zarar ya murmure.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

’Yan majalisar wakilai bakwai daga Akwa Ibom sun sauya sheka zuwa APC

Ana cigaba da samun rahotannin sauyin sheka a majalisar wakilai, yayin da ’yan majalisa bakwai daga Jihar Akwa Ibom suka koma jam’iyyar APC. Wadanda suka...

Jam’iyyar Labour tsagin Julius Abure ta ba Peter Obi sa’o’i 48 ya fice daga jam’iyyar saboda shiga hadakar ADC

Jam’iyyar Labour karkashin jagorancin Julius Abure ta bai wa tsohon dan takarar shugaban kasa, Peter Obi, wa’adin sa’o’i 48 da ya fice daga jam’iyyar, bisa...

Mafi Shahara