DCL Hausa Radio
Kaitsaye

’Yan majalisar wakilai bakwai daga Akwa Ibom sun sauya sheka zuwa APC

-

Ana cigaba da samun rahotannin sauyin sheka a majalisar wakilai, yayin da ’yan majalisa bakwai daga Jihar Akwa Ibom suka koma jam’iyyar APC. Wadanda suka sauya shekar sun hada da mutane shida daga PDP da daya daga YPP.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito kakakin majalisar cewa Tajudeen Abbas, ne ya karanta wasikun sauya shekar a zaman majalisar na ranar Alhamis, inda suka ce rikicin cikin gida na jam’iyyar PDP a matakin jiha da na kasa ne ya sa suka fice.

Google search engine

Sai dai shugaban marasa rinjaye na majalisar, Hon. Kingsley Chinda, ya bayyana bakin ciki da matakin, yana mai cewa zargin rikici a PDP ba shi da tushe, kuma bai dace da doka ba.

Abun da ya sanya ya bukaci kakakin majalisar da ya yi aiki da sashi na 68 (1) (g) na kundin tsarin mulki, ta hanyar ayyana kujerunsu a matsayin za’a sake zaben su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara