DCL Hausa Radio
Kaitsaye

’Yan majalisar wakilai bakwai daga Akwa Ibom sun sauya sheka zuwa APC

-

Ana cigaba da samun rahotannin sauyin sheka a majalisar wakilai, yayin da ’yan majalisa bakwai daga Jihar Akwa Ibom suka koma jam’iyyar APC. Wadanda suka sauya shekar sun hada da mutane shida daga PDP da daya daga YPP.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito kakakin majalisar cewa Tajudeen Abbas, ne ya karanta wasikun sauya shekar a zaman majalisar na ranar Alhamis, inda suka ce rikicin cikin gida na jam’iyyar PDP a matakin jiha da na kasa ne ya sa suka fice.

Google search engine

Sai dai shugaban marasa rinjaye na majalisar, Hon. Kingsley Chinda, ya bayyana bakin ciki da matakin, yana mai cewa zargin rikici a PDP ba shi da tushe, kuma bai dace da doka ba.

Abun da ya sanya ya bukaci kakakin majalisar da ya yi aiki da sashi na 68 (1) (g) na kundin tsarin mulki, ta hanyar ayyana kujerunsu a matsayin za’a sake zaben su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Jam’iyyar Labour tsagin Julius Abure ta ba Peter Obi sa’o’i 48 ya fice daga jam’iyyar saboda shiga hadakar ADC

Jam’iyyar Labour karkashin jagorancin Julius Abure ta bai wa tsohon dan takarar shugaban kasa, Peter Obi, wa’adin sa’o’i 48 da ya fice daga jam’iyyar, bisa...

Cibiyar taro ta Bola Tinubu ta samar da naira miliyan 650 cikin mako uku — Minista Wike

Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya bayyana cewa sabuwar Cibiyar taro ta Ƙasa da Ƙasa mai suna Bola Ahmed Tinubu da aka kaddamar kwanan...

Mafi Shahara