DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Babban kalubalen da jam’iyyar ADC za ta fuskanta shi ne zaben ɗan takarar shugaban Kasa – Datti Baba-Ahmad

-

Ɗan takarar Mataimakin shugaban ƙasa a jam’iyyar LP a zaɓen 2023, Datti Baba-Ahmed, ya bayyana ra’ayinsa kan sabuwar hadakar jam’iyyun adawa da suka ɗora kan jam’iyyar ADC.

A wata hira da aka yi da shi a tashar Arise TV ranar Alhamis, Baba-Ahmed ya ce, wannan hadaka ta ADC na da kamanceceniya da yadda aka haɗa jam’iyyun da suka kafa jam’iyyar APC a 2015, amma ya ce akwai rashin daidaito na tsari a cikin sabuwar haɗakar.

Google search engine

Ya bayyana cewa, a lokacin da aka kafa APC, an riga an ɗauki Tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari a matsayin zababben ɗan takara tun kafin zaɓen fidda gwani.

Sai dai kuma, ita wannan hadakar jam’iyyun da ta haɗa da manyan ‘yan siyasa irin su Atiku Abubakar, Peter Obi, Rotimi Amaechi da sauransu, ba ta bayyana matsayin dan takarar da zai wuce gaba a zaben 2027 ba, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ambato.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara