DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nada Ahmed Musa a matsayin manajan kungiyar Kano Pillars

-

Gwamnan Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya amince da sake fasalin hukumar gudanarwa ta ƙungiyar ƙwallon kafa ta Kano Pillars, tare da naɗa tsohon kyaftin ɗin Super Eagles, Ahmed Musa, a matsayin sabon Babban Manajan ƙungiyar.

Wannan sauyi na daga cikin matakan da gwamnatin jihar ke ɗauka domin farfaɗo da martabar ƙungiyar Kano Pillars, yayin da take shirin shiga sabuwar kakar gasar Nigeria Premier Football League (NPFL) ta shekarar 2025/2026.

Google search engine

Sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Juma’a, ta bayyana cewa an yanke wannan hukuncin ne bayan tattaunawa da masu ruwa da tsaki a harkar ƙwallon kafa, biyo bayan ƙarewar wa’adin hukumar da ta gabata wanda ya ɗauki shekara guda.

Sabuwar hukumar gudanarwar da aka ƙaddamar na da mambobi 17, inda Ali Muhammad Umar (Nayara) zai jagoranci hukumar a matsayin Shugaba, tare da sauran mambobi, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara