DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu ta umurci da a mayar da Natasha Akpoti bakin aikinta na Sanata a majalisa

-

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta umarci Majalisar Dattawa ta janye dakatarwar da ta yi wa sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, mai wakiltar Kogi ta tsakiya.

A watan Maris da ya gabata ne, majalisar Dattawa ta dakatar da Natasha na tsawon watanni shida bisa zargin rashin da’a, bayan sabani da shugaban majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, kan sauya zamanta a zauren majalisa.

Google search engine

Sanatar ta zargi Akpabio da yi mata tayin lalata, sannan ta shigar da korafi a gaban Majalisar Dinkin Duniya.

Saidai a rahoton da jaridar Daily Trust ta ruwaito mai shari’a Binta ta ce dokar ba ta fayyace adadin kwanakin da za a iya dakatar da dan majalisa ba, kuma la’akari da cewa Majalisa tana da kwanaki 181 na zama a kowace shekara, dakatar da Sanata Natasha na tsawon watanni shida kamar hana wakilcin mazabarta ne gaba daya.

Bisa wannan dalili, kotun ta umarci majalisar Dattawa da ta dawo da ita nan take domin ci gaba da wakilci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara