Wata kotun tarayya ta samu Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, mai wakiltar yankin Kogi ta Tsakiya da laifin raina kotu (contempt of court).
Kotun ta umurce ta da ta rubuta takardar neman afuwa, wadda za a wallafa a jaridu biyu na kasa da kuma shafin Facebook dinta domin ta tsarkake kanta daga laifin.
Haka kuma, kotun ta umurce ta da ta biya gwamnatin tarayya tarar Naira miliyan 5.
Gidan Talabijin na TVC ya ruwaito cewa an bayar da wa’adin kwanaki 7 don cika waɗannan sharuddan da kotu ta gindaya.



