DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sanatocin PDP biyu daga jihar Osun sun jaddada goyon bayansu ga shugaban Tinubu

-

Sanatocin jam’iyyar PDP daga jihar Osun, Sanata Adenigba Fadahunsi daga Osun ta Gabas da Sanata Olubiyi Fadeyi mai wakiltar Osun ta Tsakiya, sun sake bayyana cikakken goyon bayansu ga gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu da kuma kudirin sake neman wa’adin Mulki a 2027.

A Yayin da suke zantawa da manema labarai a Osogbo, babban birnin jihar, a ranar Alhamis, sanatocin sun yaba da irin ayyukan raya kasa da Tinubu ya kawo a mazabunsu da kuma irin jagorancin kwarai da ya nuna tun bayan hawansa Mulki.

Google search engine

Fadeyi, wanda ke shugabantar kwamitin muhalli a Majalisar Dattawa, ya ce mutanen Osun ta tsakiya za su marawa Tinubu baya da kuri’unsu a 2027.

Kazalika shima Sanata Fadahunsi cikin rahoton jaridar The Nation, ya yabawa Shugaban kasa bisa amincewarsa da ware kudade a kasafin kudin 2025 domin gyaran babban titin Ibadan zuwa Ilesa, wanda ke da matukar muhimmanci ga harkokin kasuwanci a jihar da kasa baki daya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara