DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sabuwar hadakar ADC na zawarcin Gwamna Dauda na jihar Zamfara

-

Jam’iyyar ADC reshen jihar Zamfara ya sanar da fara zawarcin Gwamna Dauda Lawal da sauran ‘yan siyasa masu nagarta a jihar na su shiga jam’iyyar, gabanin zaben 2027, kamar yadda gidan talabijin na Channels ya rawaito.

Da yake magana da manema labarai a Gusau babban birnin jihar, Shugaban jam’iyyar Kabiru Garba, ya bayyana cewa jam’iyyar ta karbi sabbin mambobi sama da 100 daga wasu jam’iyyu daban-daban cikin kwanaki goma da suka gabata, yana mai cewa sauyin sheka da aka samu ƙarfafa guiwa ne ga jam’iyyar.

Google search engine

Ya bayyana fatarsa cewa karin ‘yan siyasa daga jam’iyyun APC da PDP za su shiga ADC nan ba da jimawa ba a jihar Zamfara, yana jaddada cewa kofar jam’iyyar a bude take ga duk wanda ke da nagartaccen hali a siyasa da kuma kishin ingantaccen mulki na ya zo ya shiga.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Daga 2026 ₦500,000 kawai ɗan Nijeriya zai iya cira a banki cikin sati ɗaya – CBN

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sake fasalin dokokin cire kuɗi daga bankuna kan sabon tsarin da zai fara aiki daga watan Janairun 2026. Babban bankin ya...

Ƴan kwangila sun girke akwatin gawa a ofishin ma’aikatar kuɗin Nijeriya

‘Yan kwangila sun girke akwatin gawa a kofar shiga ofishin ma’aikatar kudin Nijeriya da ke Abuja.   ‘Yan kwangilar, karkashin inuwar kungiyarsu ta 'yan asalin Nijeriya sun...

Mafi Shahara