DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Faransa ta kammala janye dakarunta daga Senegal bayan shafe shekaru 65 a kasar

-

Gwamnatin Faransa ta kammala janye dakarunta daga ƙasar Senegal bayan shekaru 65 da girka sansanonin soja a ƙasar tun bayan samun ‘yancin kai.

A wani taron miƙa ikon da aka gudanar a Dakar, jami’an gwamnati daga Faransa da Senegal sun halarci bikin miƙa sansanin Camp Geille — mafi girma daga cikin sansanonin Faransa a ƙasar — da kuma filin tashi da saukar jiragen sama da Faransa ke amfani da shi a filin jirgin Dakar.

Matakin na zuwa ne a matsayin wani bangare na janyewar Faransa daga tsofaffin ƙasashen da ta yi wa mulkin mallakanta a Afirka, inda ƙasashe ke ƙara buƙatar ‘yanci da ikon gudanar da harkokin tsaro ba tare da tsoma bakin ƙasashen Turai ba.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara