Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf, ya bayyana cewa gwamnatinsa ta riga ta aiwatar da kashi 85 cikin 100 na alkawuran da ta dauka lokacin yakin neman zabe, yana mai cewa saura kashi 15% kacal kafin a cika kafin ya kammala mulki.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a yau Alhamis yayin rantsar da sabon shugaban ma’aikata na fadarsa, Dr Sulaiman Wali Sani, tare da shugaban hukumar ayyuka na usamman, Manjo Janar Sani Muhammad (rtd), da kuma nasu ba da shawara na musamman guda 11.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito Gwamna Abba na cewa, wannan ci gaba ya samo asali ne bayan ingantaccen nazari da kimantawa da gwamnatinsa ta gudanar cikin shekaru biyu da suka gabata.
Gwamnan ya kuma tabbatar da cewa gwamnatinsa ba za ta tsaya nan ba, domin akwai shirin kawo sabbin tsare-tsare da shirye-shirye domin ƙara inganta rayuwar al’ummar jihar.
Mun cika kashi 85 cikin 100 na alkawuranmu ga al’ummar Kano – Gwamna Abba Gida Gida
-


