DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Najeriya na cikin ƙasashe 10 a duniya da suka fi take haƙƙin ma’aikata – Binciken ICTU Global Index

-

Kungiyar Kwadago ta Nijeriya (NLC) ta bayyana rashin jin daɗinta kan yadda ƙasar ta ƙara faɗawa cikin jerin ƙasashen da ke da mummunan tarihin take haƙƙin ma’aikata a duniya.

Shugaban NLC, Comrade Joe Ajaero, wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Adewale Adeyanju, ya bayyana haka ne a lokacin taron shekara-shekara karo na 68 na ƙungiyar NECA (Nigeria Employers’ Consultative Association) da aka gudanar a birnin Lagos a ranar Laraba.

A cewarsa, sabon rahoton na ITUC Global Rights Index na 2025 ya sanya Najeriya cikin ƙasashe 10 a duniya da suka fi take haƙƙin ma’aikata.

Ajaero ya ƙara da cewa da yawa daga cikin take haƙƙin ma’aikata da rahoton ya ambata, na faruwa ne a cikin manyan kamfanoni da cibiyoyin kasuwanci da ke cikin ƙungiyar NECA.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara