DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan majalisar dokokin jihar Kebbi sun ba da gudunmuwar motoci 25 don yakin neman zaben Shugaba Tinubu a 2027

-

Kungiyoyin farar hula da jam’iyyun adawa a jihar Kebbi sun nuna rashin jin daɗinsu kan matakin da ‘yan majalisar dokokin jihar na ba da gudummawar motoci guda 25 ga ƙungiyar siyasa mai suna Tinubu/Kaura 2 Terms (TKT), wadda ke fafutukar ganin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da Gwamna Nasir Idris sun samu wa’adin mulki na biyu a 2027.

Rahotanni sun bayyana cewa motocin da aka bayar kowacce daga cikinsu na tsakanin naira miliyan 3.5 zuwa miliyan 6, bisa farashin motoci a shafin Cars45.com.

Shugaban majalisar dokokin Kebbi, Alhaji Muhammad Usman-Zuru, ne ya miƙa motocin ga ƙungiyar a madadin sauran mambobin majalisar guda 25, yana mai cewa hakan na cikin alkawarin da suka dauka lokacin da aka ƙaddamar da ƙungiyar a ranar 20 ga Mayu, 2025.

Sai dai wannan mataki ya haifar da ce-ce-ku-ce daga ‘yan adawa da masu fafutuka, inda suka zargi majalisar da cin amanar jama’a da amfani da dukiyar gwamnati don biyan bukatun siyasa.

Masu suka sun bayyana cewa bai kamata ‘yan majalisar da ke matsayin wakilan jama’a ta maida kanta ‘yan kamfen ba, musamman a lokacin da ake fuskantar matsaloli na tattalin arziki da bukatar kashe kudi a bangarori masu mahimmanci kamar lafiya, ilimi da ababen more rayuwa.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara