DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Yadda Natasha Akpoti ta kutsa majalisar dattawa duk da haramta mata shiga

-

Dakatacciyar Sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan, ta cika alkawarinta na komawa bakin aiki a majalisar dattawan Nijeriya, biyo bayan hukuncin kotu da yace a mayar da ita.

Natasha ta bayyana a harabar Majalisar Tarayya da misalin ƙarfe 12:20 na rana ranar Talata tare da gungun mutanen da suka yi mata rakiya, ciki har da fitacciyar mai rajin kare ‘yancin bil’adama, Aisha Yesufu, da wasu masu goyon bayan yunkurinta.

Sai dai, jami’an tsaro sun dakatar da Natasha daga shiga ginin babban zauren Majalisar Dattawa, duk kuwa da cewa ta bayyana a fili cewa zata dawo bakin aiki a wannan Talata.

Rahotanni sun nuna cewa an ƙara tsaurara matakan tsaro a Majalisar tun kafin zuwan Natasha, inda jami’an tsaro da suka hada da ‘yan sanda, jami’an Civil Defense, da kuma DSS suka rufe babbar ƙofar shiga majalisar, tare da tsaurara bincike.

Wannan mataki ya janyo dogon layin motoci a ƙofar shiga majalisar, yayin da jami’an tsaro ke ƙoƙarin tabbatar da cewa Natasha ba ta iya ketare shingen bincike ba.

Wasu daga cikin magoya bayan Sanatar da suka rako ta zuwa Majalisar Tarayya an ji suna rera waka da harshen Pidgin suna cewa: “Sanatar mu ce wannan, ba mu da wata sai ita,” inda wasu ke amsawa da: “Eh ita ce Sanatarmu”

Daga bisani dai Natasha, ta sauka akan motoci tare da yin tattaki domin shiga majalisar kamar yadda ta yi alkawari a baya.

Majalisar Dattawa ta riga ta yi mata kashedi da ta dakatar da yunkurin komawa aiki da karfi da yaji kafin kammala wa’adin dakatarwarta.

A gefe guda, Majalisar Dattawa ta sake jaddadawa karo na uku – cewa babu wani hukuncin kotu da ya tilasta mata dawo da Natasha bakin aiki kafin wa’adin dakatarwar ya cika.

Google search engine
Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara