DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu ba ta umarci a mayar da sanata natasha ba – Wani Lauya a Nijeriya

-

Wani lauya, Ekemini Udim, ya bayyana cewa kotu ba ta bayar da umarnin a mayar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan zauren majalisar dattawa ba, bayan dakatarwar watanni shida da aka yi mata a watan Maris.

A wata tattaunawa da aka yi da shi a gidan talabijin na Channels, Udim ya ce: “Mai shari’a bai ce a mayar da sanata Natasha ba. Abin da ya ce shi ne Majalisar Dattawa ta sake nazari kan dokokinta.”

Google search engine

Sanata Natasha, da aka dakatar bisa zargin saba dokokin majalisa da kuma furucin cin zarafi da ta yi wa shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, ta nemi komawa kujerarta ranar Talata, amma jami’an tsaro suka hana ta shiga harabar majalisa.

Bayan haka, ta bayyana rashin jin dadinta kan lamarin tare da cewa za ta tuntubi lauyoyinta domin daukar mataki na gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara