DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An yi zanga-zangar rashin tsaro a yankunan birnin Gusau na jihar Zamfara

-

Mazauna wasu yankuna da dama a karamar hukumar Gusau ta jihar Zamfara sun gudanar da zanga-zangar lumana a ranar Laraba, suna neman daukin gaggawa daga gwamnati don dakile karuwar hare-haren ‘yan bindiga a yankunansu.

Zanga-zangar, wadda ta fara da misalin karfe goma sha biyu na rana, ta hada da gungun jama’a masu yawa, wasu a kan babura, wasu cikin motoci, da kuma wasu na tafiya a kasa, suka ratsa birnin Gusau har suka isa kofar gidan gwamnatin jihar.

Google search engine

Kauyuka da suka hada da Mada, Ruwan Bore, Fegin Baza, Bangi, Lilo, Wonaka, da Fegin Mahe sun fuskanci hare-hare sau da dama, inda mazauna yankunan suka ce sama da mutum 100 ne aka kashe cikin watannin da suka gabata.

Daya daga cikin masu zanga-zangar, Malam Abubakar Abdullahi daga Fegin Mahe, ya bayyana cewa ya rasa ‘yan’uwansa da dama sakamakon rikicin, kuma an kwashe masa kaya da darajarsu ta haura naira miliyan daya daga shagonsa, ciki ha da buhunan taki guda 500.

Haka zalika, rashin tsaro ya dakile harkokin noma, inda mazauna yankunan ke cewa ya zama hadari matuka su fita noma a gonakinsu kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaba Tinubu babbar kyauta ne daga Allah domin gyaran Nijeriya – Yahaya Bello

Tsohon gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello ya bayyana shugaban Nijeriya Bola Tinubu a matsayin babbar kyauta da Allah ya ba Nijeriya domin gyaran kasar. Yahaya Bello...

Gwamnatin Nijeriya ta ce cin jarabawar lissafi “Mathematics” wajibi ne ga daliban Sakandare kafin kammalawa

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa lallai dukkan ɗalibai masu rubuta jarabawar kammala sakandare su cigaba da rubuta lissafi tare da harshen Turanci a matsayin wajibi. Mai...

Mafi Shahara