DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ba mu goyon bayan Dangote ya rika kai fetur a sassan Nijeriya – Masu jigilar man

-

Kasa da wata daya kafin fara tsarin rarraba man fetur kai tsaye daga matatar Dangote, masu jigilar fetur a Nijeriya sun bukaci kamfanin da ya janye wannan kudiri nasa.

Daga ranar 15 ga Agusta, kamfanin Dangote zai fara samar da man fetur kai tsaye zuwa gidajen mai, kamfanonin sadarwa, bangaren sufurin jiragen sama, da sauran manyan wurare masu amfani da man fetur.

Google search engine

Sai dai, masu jigilar man fetur karkashin kungiyarsu ta Natural Oil and Gas Suppliers Association of Nigeria sun bayyana damuwa cewa wannan mataki na iya haddasa asarar ayyukan yi da dama a bangaren.

A cikin wata sanarwa da aka raba wa manema labarai, Shugaban kungiyar NOGASA, Benneth Korie, ya ce shirin Dangote na kauce wa tsarin rarraba man da aka saba da shi zai kawo tangarda ga harkar samar da man fetur da iskar gas a Nijeriya, kuma zai jefa rayuwar dubban ma’aikata cikin hadari.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara