DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Cutar Tamowa ta galabaitar da yara miliyan biyu a Arewa ta Gabas da maso Yammacin Nijeriya – Jakadan Tarayyar Turai

-

Jakadan Tarayyar Turai (EU) a Nijeriya da ECOWAS, Gautier Magnot, ya bayyana cewa sama da yara miliyan biyu da ke fama da matsanancin rashin abinci mai gina jiki a yankunan Arewa maso Gabas da Arewa maso Yamma, inda suke bukatar karin abinci da magani domin ceton rayuwarsu.

Magnot ya bayyana haka ne a wata hira da ya yi da Channels Television a shirin The Morning Brief ranar Juma’a, inda ya ce janyewar taimako daga Amurka da wasu abokan hulda ya bar gibi mai girma, a kokarin tallafawa wadannan yara da abincin tamowa da suka dogara da shi.

Ya ce akwai bukatar gaggauta daukar mataki domin cike gibi da kuma kare rayukan yaran da ke cikin hadari matuka sakamakon yunwa da rashin abinci mai gina jiki.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara