DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jagororin majalisar dattawa Akpabio da Bamidele sun samu rashin jituwa kan salon jagoranci

-

Rashin jituwa ya kunno kai a cikin shugabancin majalisar dattawan Najeriya, biyo bayan sabani da ya fito a fili tsakanin Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, da Jagoran Majalisar, Opeyemi Bamidele, kan salon jagorancin Akpabio, kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito.

Rigimar da ta faru a zaman majalisa na ranar Laraba ita ce sabuwar alamar rikici da ke ci gaba da dabaibaye zauren majalisar, musamman tsakanin manyan kusoshin jam’iyyar APC mai mulki.

Ko da yake an sha musanta labaran da ke nuna akwai rikici a cikin shugabancin majalisar, majiyoyi sun bayyana cewa sabanin da ya biyo bayan zaben Akpabio a matsayin shugaban majalisar a 2023 har yanzu yana nan.

Wasu daga cikin manyan ’yan majalisar na bayyana damuwa a sirrance kan yadda suke kallon salon jagorancin Akpabio a matsayin mai danniya da fifita kansa.

Google search engine
Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaba Tinubu babbar kyauta ne daga Allah domin gyaran Nijeriya – Yahaya Bello

Tsohon gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello ya bayyana shugaban Nijeriya Bola Tinubu a matsayin babbar kyauta da Allah ya ba Nijeriya domin gyaran kasar. Yahaya Bello...

Gwamnatin Nijeriya ta ce cin jarabawar lissafi “Mathematics” wajibi ne ga daliban Sakandare kafin kammalawa

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa lallai dukkan ɗalibai masu rubuta jarabawar kammala sakandare su cigaba da rubuta lissafi tare da harshen Turanci a matsayin wajibi. Mai...

Mafi Shahara