DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jihohin da ke son rage kudin wutar lantarki dole su biya tallafi – Hukumar NERC

-

Hukumar kula da lantarki ta Nijeriya (NERC) ta bayyana cewa gwamnatocin jihohi ba su da ikon mallakar rumbun wutar lantarki ta kasa (national grid) ko kuma tashoshin wutar lantarki da aka kafa bisa dokokin tarayya ko wadanda ke aiki da lasisin da hukumar ta bayar.

Hukumar ta fadi hakan ne a cikin wata sanarwa da ta fitar domin mayar da martani kan cece-kuce da ya biyo bayan matakin Hukumar Lantarki ta Jihar Enugu da ta rage kudin wutar Band A.

A cikin wata sanarwa a ranar Alhamis, hukumar NERC ta bukaci gwamnatocin jihohi da su sanya farashin wutar da ya yi daidai da kudin sayen wutar gaba daya ko kuma su shirya su biyan tallafi idan suka rage farashin fiye da yadda ya kamata.

Google search engine
Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara