DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jihohin da ke son rage kudin wutar lantarki dole su biya tallafi – Hukumar NERC

-

Hukumar kula da lantarki ta Nijeriya (NERC) ta bayyana cewa gwamnatocin jihohi ba su da ikon mallakar rumbun wutar lantarki ta kasa (national grid) ko kuma tashoshin wutar lantarki da aka kafa bisa dokokin tarayya ko wadanda ke aiki da lasisin da hukumar ta bayar.

Hukumar ta fadi hakan ne a cikin wata sanarwa da ta fitar domin mayar da martani kan cece-kuce da ya biyo bayan matakin Hukumar Lantarki ta Jihar Enugu da ta rage kudin wutar Band A.

A cikin wata sanarwa a ranar Alhamis, hukumar NERC ta bukaci gwamnatocin jihohi da su sanya farashin wutar da ya yi daidai da kudin sayen wutar gaba daya ko kuma su shirya su biyan tallafi idan suka rage farashin fiye da yadda ya kamata.

Google search engine
Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaba Tinubu babbar kyauta ne daga Allah domin gyaran Nijeriya – Yahaya Bello

Tsohon gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello ya bayyana shugaban Nijeriya Bola Tinubu a matsayin babbar kyauta da Allah ya ba Nijeriya domin gyaran kasar. Yahaya Bello...

Gwamnatin Nijeriya ta ce cin jarabawar lissafi “Mathematics” wajibi ne ga daliban Sakandare kafin kammalawa

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa lallai dukkan ɗalibai masu rubuta jarabawar kammala sakandare su cigaba da rubuta lissafi tare da harshen Turanci a matsayin wajibi. Mai...

Mafi Shahara