DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ana fargabar mutane da dama sun nutse sanadiyyar kifewar jirgin ruwa a Neja

-

Rahoton jaridar The Nation ya ce mutane da dama, ciki har da mata da yara, sun rasu yayin da wani karamin jirgin kwale-kwale na katako ya nutse a kogin Shiroro da ke karamar hukumar Shiroro a Jihar Neja a ranar Asabar.

Wani ganau ya bayyana cewa jirgin ya taso daga Guni yankin rafi a karamar hukumar Munya zuwa kasuwar Asabar da ke ci a Zumba, inda ya nutse da misalin karfe 2:30 na rana bayan ya ci karo da wata bishiya da ke cikin ruwa.

Google search engine

Rahotanni sun ce an makare jirgin da fasinjoji da kaya, saidai ana ci gaba da aikin ceto, amma har yanzu ba a san yawan adadin wadanda suka rasu ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara