DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ka fito ka baiwa Tinubu haƙuri kan zargin nuna bambanci a ayyuka – Sakon ministan ayyuka ga Kwankwaso

-

Ministan ayyuka na Nijeriya, David Umahi, ya bukaci tsohon Gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, da ya baiwa Shugaba Bola Ahmed Tinubu haƙuri, bisa zargin da ya yi cewa gwamnatin Tinubu na fifita kudancin Najeriya fiye da arewa wajen rabon ayyukan raya ƙasa.

A wata sanarwa da Umahi ya fitar, wadda mai ba Shugaba Tinubu shawara kan bayanai da dabarun sadarwa, Bayo Onanuga, ya wallafa a dandalin X, ministan ya ce zargin Kwankwaso “ba daidai ba ne rudani ne na siyasa.”

Google search engine

Gidan talabijin na Channels ya Ambato ministan ya ce a gaskiya, Shugaba Tinubu ya fi mai da hankali wajen raya Arewacin Najeriya, musamman Arewa maso Yamma — yankin da Kwankwaso ya fito, fiye da Kudu.

Ya buga misalin manyan ayyukan da ke gudana a Arewacin Najeriya akwai mai tsawon kilomita 1,068 daga Sokoto zuwa Badagry, wanda ya bayyana a matsayin gagarumin aikin da zai haɗa Arewaci da Kudanci da hanya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara