A yayin kaddamar da kwamitin binciken mai ƙarfi wanda zai gudanar da cikakken bincike kan lamarin, gwamnan ya bayar da wa’adin mako guda kacal domin gano gaskiyar al’amari tare da bayar da rahoto.
Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Alhaji Umar Faruk Ibrahim ne ya wakilci Gwamnan wajen kaddamar da kwamitin, inda ya bayyana cewa wannan mataki na cikin kudirin gwamnatin Kano na yaki da miyagun ƙwayoyi da kuma tabbatar shugabanci na gari.
Sakataren Gwamnati ya ce an zaɓi mambobin kwamitin ne bisa cancanta, ƙwarewa, jajircewa da ƙwarin guiwar cika alƙawarin da aka ɗora musu.
A madadin sauran mambobin, shugaban kwamitin, Barrister Aminu Hussaini, ya gode wa Gwamnatin Kano bisa daukar matakin gaggawa, tare da alkawarin gudanar da aikinsu cikin gaskiya, riƙon amana da kwarewa.



