By Salisu Ado Sulaiman
Hukumar wayar da kan al’umma ta Najeriya NOA ta yi hasashen cewa kasar na dab da wuce kasar Algeria wajen zama ta uku mafi karfin tattalin arziki a nahiyar Afirka a 2025 da muke ciki.
Hukumar ta NOA, wacce ministan yada labaran Najeriya Alhaji Muhammad Idris ke jagoranta, ta nuna cewa kasar ta samu bunkasar tattalin arziki da kaso 38 bisa ma’aunin GDP, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
Wani rahoton mako da hukumar ta wallafa, ya nuna cewa tattalin arzikin Najeriya ya kai Naira Tiriliyan 372.8 bisa ma’aunin GDP, daga shekarar 2019 zuwa 2024.



