DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tulin bashi na iya tilasta gwamnatin Nijeriya janye tallafin lantarki – Tsohon Shugaban NERC

-

By Salisu Ado Sulaiman

Tsohon shugaban hukumar kula da wutar lantarki na Najeriya Sam Amadi, yace tulin bashi na iya zama sanadiyyar da gwamnatin tarayya za ta janye tallafin da take zubawa a bangaren.

Amadi ya bayyana haka ne a tattaunawar sa da gidan talabijin na Channels, sai dai ya ce muddin gwamnatin tayi haka ba dabara bace, duba da yadda kasashen da suka ci-gaba ke samar da wutar lantarki a farashi mai rahusa.

Kan matsalar ta wutar lantarki da Najeriya ke fama da ita, tsohon shugaban hukumar ya nuna damuwa da irin rawar da rashin kayan aiki masu inganci da kuma cin hanci da rashawa ke takawa.

Google search engine
Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara