DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ƴan bindiga sun yi ajalin mutane 38 duk da sun karbi Naira miliyan 50 a Zamfara

-

Wasu ƴan bindiga sun yi ajalin mutane 38 daga ƙauyen Banga, karamar hukumar Kauran-Namoda ta jihar Zamfara, duk da cewa an biya su kuɗin fansa fiye da Naira 50 miliyan.

Shugaban karamar hukumar Kauran -Namoda, Mannir Haidara Kaura, ya tabbatar da cewa 56 ne aka sace, amma 18 daga ciki ne kacal suka dawo a raye bayan biyan fansar.

Google search engine

Ya ce an kwantar da waɗanda suka dawo a asibiti domin samun kulawar likitoci, kana gwamnatin jihar tana shirin ziyartar iyalan waɗanda suka rasu sakamakon waki’ar.

Rahoton gidan talabijin na Channels ya ce wani mazaunin ƙauyen, Ibrahim Banga, ya bayyana cewa ƴan bindigar sun nemi Naira miliyan 1 a kan kowanne mutum, amma bayan biyan kuɗin, sai suka kashe sauran 38 cikin zalunci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara