DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan Zamfara ya naɗa Alhaji Abdulkadir Ibrahim Bello a matsayin sabon Sarkin Katsinan Gusau

-

Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara ya amince da nadin Alhaji Abdulkadir Ibrahim Bello a matsayin Sarki na 16 na Masarautar Gusau, wanda ya gaji mahaifinsa, Marigayi Dr. Ibrahim Bello, da ya rasu a ranar 25 ga Yuli bayan shekaru goma yana sarauta.

A cewar wata sanarwa da ofishin sakataren gwamnatin jihar ya fitar, nadin ya biyo bayan shawarwarin masu zaben sarki na masarautar Gusau, tare da bin al’adun gargajiya da dokoki na kasa.

Alhaji Abdulkadir, wanda shi ne babban ɗan marigayim, yana rike da sarautar Bunun Gusau kafin wannan nadin.

Shi ɗan asalin Malam Sambo Dan Ashafa ne.

Gwamna Dauda Lawal ya taya sabon sarki murna tare da kira gare shi da ya ci gaba da gadon kyakkyawar rayuwa da dabi’un sarakunan da suka gabata, wanda zai zama jigo wajen ɗorewar zaman lafiya, haɗin kai da ci gaba a masarautar Gusau da kewaye.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara