DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin tarayya na iya sake sayar da kamfanonin raba wutar lantarki 11 a Nijeriya

-

Gwamnatin Tarayya na iya sake sayar da kamfanonin raba wutar lantarki guda 11 (Discos) idan kudirin gyaran dokar lantarki na 2025 ya zama doka.

Kudirin, wanda Sanata Enyinnaya Abaribe ya dauko, na nufin tilasta wa kamfanonin su saka sabon jari cikin shekara guda ko kuma su fuskanci hukunci irin su karancin hannun jari, kwace ko sake cefanarwa.

Google search engine

Jaridar Punch ta tattaro cewa majalisa ta ce matakin zai koma bayan da aka samu tun bayan dokar 2023. Sai dai kungiyar kwamishinonin makamashi ta soki kudirin, tana cewa hakan na iya rusa cigaban da aka samu a sabon tsarin kasuwancin wutar lantarki.

Yanzu haka dai kamfanonin Discos 11 da abin zai shafa sun hada da na Abuja, Benin, Eko, Enugu, Ibadan, Ikeja, Jos, Kaduna, Kano, Port Harcourt da Yola.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara