DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hare-haren ta’addanci na raguwa a jihar Katsina zamanin mulkin Tinubu – Wazirin Katsina, Ibrahim Ida

-

Wazirin Katsina, Ibrahim Idah, ya bayyana cewa hare-haren ‘yan ta’adda sun ragu matuƙa a ƙarƙashin mulkin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, musamman a jihar Katsina.

Da yake jawabi a taron haɗin gwiwa tsakanin gwamnati da shugabannin Arewa, Idah ya ce Tinubu ya cika alkawarin yaƙi da bazuwar makamai, wanda hakan ke haifar da raguwar hare-hare idan aka kwatanta da shekarun baya kamar yadda jaridar Premium Times ta sanar.

Google search engine

Ya kuma buƙaci a karfafi rundunar tsaron sa-kai da makamai masu ƙarfi domin ƙarfafa tsaro, sai dai shugaban NDLEA, Buba Marwa, ya ja kunne kan haɗarin hakan, yana mai ba da misalin wani kwamandan sa-kai a Borno da ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi tare da zuwa ofishin hukumar da mayaka fiye da 50.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara