DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ku jira sai zuwa 2031 tukuna – Shawarar George Akume kenan ga ‘yan siyasar Arewa da ke neman kujerar shugaban kasa

-

Sakataren Gwamnatin Tarayyar Nijeriya, Sanata George Akume, ya shawarci ‘yan siyasa daga yankin Arewa da su dakata har zuwa shekarar 2031 kafin su nemi kujerar shugaban kasa.

Akume ya bayyana haka ne a ranar Talata yayin wani taron tattaunawa na kwanaki biyu a Kaduna, wanda aka shirya domin karfafa hulɗa tsakanin gwamnati da ‘yan ƙasa.


Jaridar Punch ta ruwaito Akume na yabawa cibiyar Sir Ahmadu Bello bisa samar da dandalin tattaunawa domin inganta shugabanci da dimokuraɗiyya a ƙasar.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Wike ya musanta jita-jitar tsayawarsa takarar shugabancin Nijeriya a zaben 2027, ya jaddada goyon bayansa ga Tinubu har zuwa 2031

Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya karyata rahotannin da ke cewa wasu jiga-jigan jam’iyyar PDP na matsa masa lamba domin ya tsaya takarar shugaban ƙasa a...

Sau 22 ana yunkurin lalata mana matatar mai – Matatar man fetur ta Dangote

Kamfanin matatar mai ta Dangote ya bayyana cewa tun bayan da matatar man da ke fitar da ganga 650,000 a rana ta fara aiki, aƙalla...

Mafi Shahara