DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Akwai wariya ga Arewacin Najeriya a gwamnatin Tinubu — Bashir Dalhatu

-

Kungiyar Arewa Consultative Forum (ACF) ta bayyana damuwarta kan yadda yankin Arewa ke fuskantar wariya wajen rabon kasafin kuɗi da aiwatar da manyan ayyuka a gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.

Shugaban kwamitin amintattu na ACF, Alhaji Bashir M. Dalhatu, ne ya bayyana haka a taron tattaunawa da Sir Ahmadu Bello Memorial Foundation ta shirya a Kaduna.

Google search engine

Dalhatu ya ce abin takaici ne ganin yadda ake yi wa yankin Arewa watsi da muhimman ayyukan ci gaba duk da irin gudunmuwar da yankin ya bayar wajen nasarar Tinubu a zaben 2023.

Ya jaddada cewa wannan lamari rashin adalci ne ga yankin da ya taka muhimmiyar rawa wajen kafa wannan gwamnati.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An gudanar da addu’o’in neman tsari daga hare-haren ‘yan bindiga a jihar Neja

Mazauna yankin jihar Neja ta Arewa sun gudanar da addu’o’i na musamman a filin Idi da ke Kontagora, hedkwatar karamar hukumar Kontagora, domin neman taimakon...

‘Yan siyasa a Nijeriya sun fi maida hanakali kan siyasa maimakon magance matsalolin al’umma – Sarkin Onitsha

Sarkin Onitsha, Igwe Nnaemeka Achebe, ya caccaki ‘yan siyasa bisa mayar da hankali kan siyasa maimakon gudanar da mulki yadda ya kamata tun kafin zaben...

Mafi Shahara